A Netherlands sakamakon farko na zaben kasar da aka yi jiya Laraba, ya nuna jam'iyyar Fara Ministan kasar Mark Rutte's, ta lashe kujeru mafi yawa a majalisar dokokin kasar, ta doke jam'iyyar dake adawa da baki da kuma addinin Islama ta dan kishin kasa Geert Wilders, da rata mai yawa wadda ba'a yi zaton tazarar ta kai haka ba.