Kwamitin jin Korafin Jama'a na Majalisar Waklilan Najeriya ya sake gayyatar mai kwarmato Dr. George Uboh kan bahasi na zambar kudin shiga sama da dala biliyan 25 daga kamfanonin man kasashen ketare.
Kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah ta ce kimanin kashi 15-20% na Fulani makiyaya na Najeriya na ficewa daga kasar zuwa tudun mun tsira.
Yayin da ake ta korafe korafe a arewacin Najeriya game da zargin rashin kulawa da yankin, wasu 'yan yankin sun ce a gaya ma Shugaba Buhari cewa sun fa gaji da gafara sa, ba su ga ko kaho ba.
Yayin da ake haramar rantsar da sabon Shugaban Kasa a Amurka yau, masana na cigaba da fashin baki yayin da kuma sauran jama'a ke cigaba da bayyana ra'ayoyinsu kan wannan rana da kuma bukin.
Ana shirin rantsar da sabuwar gwamnati a Amurka, bayan zabe da aka gudanar a watan Nuwamban Bara.
A ci gaba da dauke hankalin duniya da abkawa Majalisar Dokokin Kasar Amurka da kuma tsige Shugaba Donald Trump karo na biyu da ya biyo baya, masana harkokin siyasar duniya na ci gaba da tsokaci game da tasirin wannan al'amarin.
Masana sun lura cewa ba za a yi sanyi a lokacinsa ba a Najeriya saboda dumamar yanayi, al'amarin da ya canza abubuwan da mutane su ka saba yi a lokacin na sanyi. Haka zalika, sun lura cewa hamadar Sahara na dannowa.
Bayan da 'yan Najeriya su ka yi ca, gwamnatin kasar ta janye shirin da aka yi zargin cewa karin kudin wutar lantarki ne a fakaice ta wajen rabewa da bangare mai zaman kansa.
Hukumar kula da farashin lantarki ta Najeriya ta ce kai tsaye ba ta kara farashin wuta da kashi 50 cikin 100 ba, amma an samu kari na wani kaso ga azuzuwan masu amfani da wuta biyar.
Kotu ta sake tura Omoyele Sowore, gidan jiran hukunci, akan zargin shi na tada zaune tsaye.
Wasu rahotanni na nuni da cewar sai da aka biya zunzurutun kudade kamun aka sako daliban Kankara.
A daidai lokacin da Majalisar Wakilan Najeriya ke jiran bayyanar shugaban kasa gabanta yau Alhamis, domin amsa tambayoyi game da halin tabarbarewar tsaro da kasa ke ciki, Ministan Shari’a ya ce bayanin Buhari ga Majalisa na iya amfanar ‘yan bindiga
Shahararren mai kwarmaton nan na Najeriya, Dr. George Uboh, ya sami gayyatar Majalisar Wakilan Najeriya don ba da bahasi kan zargin salwantar kudi sama da dala Biliyan 35 a ma'ajiyar gwamnatin tarayya.
Yayin da gwamnatin Najeriya ke nazarin yiwuwar sake bude kan iyakarta don hada hadar cinakayya da sauransu, 'yan kasar sun shiga muhawara kan alfanu da kuma rashin alfanun yin hakan.
Mako daya bayan sace daliban sashen Faransanci na jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria su tara,da wasu mutane da masu satar mutane su ka yi a hanyar Kaduna zuwa Abuja, an samu nasarar sako su bayan biyan kudin fansa.
'Yan bindigar da suka sace daliban Sashen Harshen Faransanci na Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja ranar Lahadi, na neman kudin fansa Naira miliyan 450 daga wajen ‘yan uwan daliban.
A cigaba da tattaunawa da 'yan Najeriya ke yi kan matsalar kuntata ma jama'a da 'yan sanda na musamman kan yi, an bukaci a yi garanbawul ma tsarin aikin 'yan sanda gaba daya, ba SARS kawai ba.
Tun rasuwar marigayi mai yaki da miyagun barayi, Alhaji Ali Kwara a ke ci gaba da nuna juyayin rashin sa, inda kafafen sadarwar yanar gizo su ka cika makil da ta'aziyar rasuwar mutumin da a ke aiyanawa a matsayin mai Jarumi.
Tsohon gwamnan jihar Sokoto da ke arewacin Najeriya, Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya ce yana jagorantar wani shiri na tattara bayanan asarar rayuka da dukiya da al'ummar arewa suka yi don neman diyyar da ta kai Naira tiriliyan bakwai.
Kungiyoyin tallafawa marayu da zawarawa da su ka hada da matan da mazajen su su ka rasu, karkashin inuwar kwamitin marayu na JIBWIS, sun yaye matan da a ka koyawa sana'a don dogaro da kai.
Domin Kari