NFF ta nada Mr. Augustine Eguavoen a matsayin kocin wucin gadi a cewar wata sanarwa da hukumar ta fitar.
Ibrahimovic, wanda dan asalin kasar Sweden ne, ya shiga wannan rukunin ne bayan da ya zura kwallonsa a karawar da suka yi da Udinese a gasar Serie A ta Italiya.
Ana sa ran Blinken zai gabatar da wani jawabi kan dagantakar Amurka da nahiyar Afirka sannan zai gana da ‘yan kasuwa a fannin fasahar zamani ta yanar gizo a birnin na Abuja.
Sai dai ministan ya ce suna da bayanan yatsun dukkan fursunonin kasar, fasahar da ya ce yana fatan za ta taimaka wajen kama fursunonin.
Shugaban Najeriya ya yi wadannan kalaman ne yayin da matsalar rashin tsaro a kasar ke ci gaba da ta'azzara, ko da yake hukumomin kasar sun ce suna shawo kan lamarin.
“Darasin da muka koya daga annobar nan, ya sa mun kara kaimi wajen magance illolin da annobar ta haifar.” In ji Buhari
Paris Saint Germain ta ce tana bibiyar lamarin tare da shan alwashin daukan matakin da ya dace a karshe.
Lamarin ya faru ne a daren ranar Talata inda ‘yan bindigar dauke da muggan makamai suka far wa yankunan na Batsari suka rika bi gida-gida suna kai hari.
"An mika ta ga jami'an tsaro don su dauki matakin da ya dace, saboda hakan ya zama aya ga sauran baragurbi." Sanarwar ta ce.
Shugaban ya kuma nuna sha’awarsa ta ganin sun yi aiki tare don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban jihar Anambra da Najeriya baki daya.
A cewar Nwankpo, bisa zabin kansa ne ya yanke shawarar jefa kuri’arsa ga Soludo saboda ya san jam’iyyarsa ba za ta kai labari ba.
Alkali Abang ya ce albashi da sauran alawus-alawus din Maina bai isa ya kai ga tara wadannan kudade ba.
Izuwa lokacin hada wannan rahoto, an kidaya kananan hukumomi tara. cikin 21 da jihar ta Anambra ke da su.
“Ina so na sanar da ku cewa wannan murabus da na yi, na yi shi ne bisa radin kaina. Ina kuma godiya ga gwamna Yahaya da ya ba ni wannan damar ta yin aiki a gwamnatinsa.” In ji Dr Hussaina
Sakamakon wannan wasa ya ba City damar matsawa zuwa matsayi na biyu a teburin gasar ta Premier.
Babu dai wani rahoto da ya nuna cewa an samu wata tangarda ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, illa ‘yar matsalar na’ura da aka samu a wasu rumfunan zabe a sassan jihar.
Farfesa Osinbajo ya ce ya mika wannan batu ga lauyoyinsa don su dauki matakin da ya dace.
Ya zuwa yanzu, mutum tara aka ceto da ransu, mace daya da maza takwas a cewar hukumomin jihar ta Legas.
Kazalika kungiyar ta PSG ta bayyana cewa Marco Verratti, shi ma bai zai buga wasan ba, saboda yana kan murmurewa daga wata jinya.
Domin Kari