Naira Marley da Sam Larry sun sha musanta hannu a mutuwar MohBad, wanda ya rasu cikin wani yanayi mai sarkakiya.
Kwantiragin Osimhen zai kare a shekarar 2025, amma akwai rahotanni da ke nuna cewa mai yiwuwa ya bar Napoli a watan Janairu.
Jama’a da dama na ta dora alhakin mutuwar Mohbad akan Naira Marley wanda shi ne tsohon maigidansa da ya fara daukansa a aiki a kamfaninsa na Marlians. Naira Marley ya musanta zargin.
Baya ga shirin “Tinsel” sauran fitattun fina-finan da Charles ya fito, sun hada da “Last Flight To Abuja,” da “Impossible Relationships,” da “Dowry Man.”
Shugaba Tinubu ya yi Allah wadai da sace daliban a wata sanarwa da kakinsa, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Lahadi.
Sojojin Nijar sun yi maza sun yi lale marhabin da wannan sanarwa ta Macron wacce suka kwatanta a matsayin “sabon babin ‘yartar” da kasarsu.
An ji mutanen da suka yi dandazo a babban zauren otel din Espinas Palace, suna ta ambaton sunan Ronaldo.
Sannan a ranar Litinin din da ta gabata Amurkawa suka yi tarukan tunawa da harin 11 ga watan Satumba da aka kawo Amurka, harin da ya yi sanadin mutuwar dubban mutane – a wannan karo harin ya cika shekara 22 da aukuwa.
Akaron farko tun bayan annobar korona, shugaba Kim Jong Un ya kai ziyarar aiki Rasha inda ake sa ran kasashen biyu za su sabunta dangantakar kawance tsakaninsu.
Za a sake wani gwajin na biyu domin tabbatar da na farko, idan kuma har aka samu Pogba da laifi, zai iya fuskantar hukuncin haramcin buga wasa na tsawon shekara hudu.
Rubiales ya kuma sanar da ajiye aikinsa na hukumar UEFA inda yake rike da mukamin mataimakin shugaban hukumar.
Hatsarin ya faru ne da misalin karfe takwas na safiyar ranar Lahadi yayin da mutanen ke kan hanyarsu ta zuwa gonakinsu, a cewar hukumomi.
Bayanai sun yi nuni da cewa, jama’ar da wannan ibtil’in ya shafa sun kwashe kwana uku suna kwana a tituna.
Bayanai sun yi nuni da cewa akalla mutum uku sun rasa rayukansu a jihohin yayin da kusan mutum dubu 500 suke zaune babu wutar lantarki.
Kazalika shirin ya duba martanin da Shugaban Amurka Joe Biden ya mayar bayan da ya samu labarin mutuwar shugaban dakarun haya na kamfanin Wagner, Yevgeny Prigozhin a Rasha.
Ana fargaban shugaban sojojin haya na Wagner Yevgeny Prigozhin ya mutu a wani hatsarin jirgin sama da ya faru a Rasha a ranar Laraba.
Alison-Maduke ta rike mukamin ministar mai a zamanin mulkin tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan daga 2010 zuwa 2015.
A ranar 25 ga watan Agusta, ake sa ran shugaban Amurka da mukarrabansa 18 za su mika kansu ga hukumomin jihar Georgia da ke Amurka don a tuhume su kan laifukan da ake zargin sun aikata
Fitar da sanarwar ma'aikatun da ministocin za su jagoranta na zuwa ne bayan da majalisar dattawa ta kammala tantance su makonnin da suka gabata.
Ganawar tasu na zuwa ne yayin da ECOWAS ke duba zabin daukan matakin soji a kan masu juyin mulki.
Domin Kari