Yayin da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ja kunnen masu yunkurin tada fitina a jihar, kwarraru da ke sharhi kan harkokin tsaro sun ankarar da al’umma game da wasu muhimman al’amura da suka shafi shiga cikin harkokin tarzoma.
Kotun Daukaka Kara ta sake jaddada nasarar Gawuna bayan yaduwar wata jita jita.
Fitar da wani sashi na daftarin hukuncin kotun daukaka kara ta Najeriya dake Abuja, dangane da shari’ar zaben gwamnan Kano ya sake dumama yanayin siyasar jihar, dai dai lokacin da masana dokoki da shari’a da kuma manzarta a fagen dimokaradiyya ke bayyana albarkacin bakin su.
Gwamnatin jihar Kano ta jam’iyyar NNPP ta ce za ta je kotun koli, bayan da kotun daukaka kara da ke Abuja ta ce dan takarar jam’iyyar APC Nasiru Yusuf Gawuna ne ya yi nasara a zaben gwamnan Kano daya gabata, kamar yadda kotun sauraren kararrakin zabe ta Kano ta yanke hukunci a kwanakin baya.
Yajin aikin da kungiyar kwadagon Najeriya NLC ta fara a daren jiya litinin ya gurgunta harkokin karatu a makarantun gwamnati na jihar Kano. Makarantun sakandare dana kwalejojin ilimi mai zurfi da kuma Jami’o’i mallakar gwamnatin jihar da na tarayya sun kasance a kulle a yau talata.
Yayin da tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya roki Majalisar Dokokin kasar ta shafe dokar da ta bada damar gudanar da zabukan gwamnoni na bai daya a Najeriya, yanzu haka masana dokoki sun fayyace hanyoyin da majalisar ka iya bi domin cimma nasara.
Al’amura sun tsaya cik a majalisun dokokin jihohi 36 na Najeriya tun bayan da ‘yayan kungiyar ma’aikatan Majalisun suka tsunduma yajin aiki a shekaranjiya Litinin. Sai dai masu sharhi na cewa yajin aikin ba shine mafita ba.
Kungiyar, mai suna WANDA Organization mai rajin bunkasa ilimin 'ya 'ya mata akan nazarin kimiyyar sarrafa abinci da samar da shi, ta dauki nauyin karatun dalibai 30 dake karatu a Jami’ar Bayero Kano wadanda ke nazari a fannin kimiyyar sarrafa abinci da dangoginsa.
Tun a farkon shekara ta 2022 ne gwamnatin Najeriya ta amince tare da ba da kwangilar gina layin dogo daga Dutse zuwa Kano da kuma Kano zuwa Maradi a Jamhuriyar Nijar, da nufin habaka harkokin sufuri da na hada-hadar kasuwanci a tsakanin Najeriya da Nijar.
Yayin da aka shiga mako na 2 da barkewar sabon fada tsakanin Isra’ila da Hamas, Zauren Malaman Addinin Musulunci na Najeriya ya bayyana rashin jin dadi kan abubuwan dake faruwa a can, a hannu guda kuma masana sun ce rashin mutunta kudurorin majalisar dinkin duniya suka sa yakin ke ci gaba da faruwa.
Wasu dalilan da suka sa a farkon makon nan kungiyoyin ‘yan kwadago a Najeriya suka janye shirinsu na shiga yajin aikin gama-gari wanda suka so farawa daga ranar 3 ga watan Oktoba
Yayin da ‘yan Najeriya ke ci gaba da kokawa dangane da tsadar albarkatun mai biyo bayan cire tallafin gwamnati tun kimanin watanni biyar da suka shude, masu gidajen man a yankin arewacin kasar sunce harkokinsu na fuskantar barazanar durkushewa, amma masana tattalin arziki sun ce akwai mafita.
Domin Kari