Wani tsohon madugun 'yan tawaye kuma dan siyasa a Jamhuriyar Nijar ya kaddamar da wani yunkuri na fafatawa da sojojin da su ka yi juyin mulki a ranar 26 ga watan Yuli, lamarin da ke zama wata alama ta farko ta adawar cikin gida da mulkin soja a wannan kasa mai matukar muhimmanci a yankin Sahel.
Sojojin da suka yi juyin mulki a jamhuriyar Nijer sun nada Ali Mahaman Lamine Zeine a matsayin Firai Ministan Gwamnatin rikon kwaryar da suke shirin kafawa a dai dai lokacin da karamar sakatariyar Amurka mai kula da harakokin siyasa Victoria Nuland ta kai ziyara a Nijar.
Wassu mata da suka yi zanga-zanga jiya Litinin a garin Mangu na jihar Filato, da ke fama da tashin hankali sun zargi jami’an soji da wuce gona da iri, da kashe wani matashi.
Amurka, yau Talata, ta goyi bayan yunkurin da kasashen yammacin Afirka ke yi na maido da tsarin mulki a Nijar bayan juyin mulkin da aka yi a ranar 26 ga watan Yuli, ta kuma ce matakin diflomasiyya ya fi amfani da karfin soja.
‘Yan Najeriya mazauna Nijar sun yi taro da nufin gamsar da ‘yan kasar ta Nijar tasirin kasar, da ma karfin huldar da ke tsakanin kasashen, su na masu bayyana cewa ba da sunansu kungiyar CEDEAO ta bai wa sojojin Nijar wa'adi ba.
‘Yan Najeriya mazauna yankunan da ke daura da iyakokin Jamhuriyar Nijar na ci gaba da zaman rashin tabbas kan abin da ka iya biyo bayan wa'adin da kungiyar ECOWAS ta bayar ga gwamnatin mulkin soji da suka hambarar da gwamnatin farar hula a kasar.
Wata hira ta musamman da wani mai sharhi a kan al'amuran yau da kullum a Nijar game da rashin Zartas da kudurin CEDEAO.
Ingila ta doke Najeriya da ci 4-2 a bugun daga kai sai mai tsaron gida a yau Litinin, inda ta samu nasarar tsallakewa zuwa matakin daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin kwallon kafa ta mata ta FIFA, wadda Australia da New Zealand ne masu masaukin baki.
Matakin rufe iyakokin ya kawo cunkoson manyan motoci makare da kaya wadanda ke son shiga Nijar amma babu dama.
Ana sa ran wannan aiki zai samar da Megawatt 350 cikin 1, 350, wanda ya kasance kashi na farko na baki dayan aikin.
Gwamnatin mulkin sojan ta Nijar, ta sallami wasu jakadun kasar da suka hada da na Amurka, Faransa, Najeriya da Togo.
Akan dambarwa dake faruwa a Nijar, mun samu tattaunawa da jakadan Nijar din anan Amurka, Mamadou Kiari Liman-Tinguiri, mun kuma duba taron gaggawa da Kungiyar ECOWAS ta yi a Abuja, Najeriya, da wasu rahotanni.
Jagoran sojojin da suka yi juyin mulki ya yi wannan ikirarin ne a wani lokacin da ake jiran zuwan tawagar ECOWAS/CEDEAO karkashin jagorancin Janar Abdulsalami Abubakar domin samo bakin zaren wannan rikici cikin ruwan sanyi.
Haka kuma majalisar sojojin ta sanar da bude iyakokin kasar ta Nijar da wasu kasashen da ba su da alaka da ECOWAS.
Domin Kari