A yau Juma’a hafsoshin sojojin kasashen yammacin Afirka suke zaman tattaunawa a rana ta biyu kuma ta karshe a birnin Accra, na Ghana, inda suka yi ta tofa albarkacin bakinsu kan yiwuwar amfani da karfin soja a Nijar, idan har tsarin diflomasiyya ya kasa kawo karshen juyin mulkin da sojoji suka yi.