Mahaifiyar Melanie Trump, matar tsohon Shugaban kasar Amurka Donald. Trump, Amalija Knavs, ta rasu, kamar yadda Trump ya tabbatar a wata sanarwa da aka wallafa a X, wanda a da ake kira Twitter. Amalija ta rasu tana da shekaru 78.
Wadanda aka sallama sun hada da Babatunde Irukera, shugaban hukumar kula sahihancin ayuka da kayayyaki (FCCPC), da Alexander Okoh, shugaban hukumar kula da harkokin gwamnati (BPE).
Jami’ai a Pakistan sun haifar da cikas ga hawa yanar gizo da toshe kafar shafukan sadarwar zamani a kasar baki daya a yammacin jiya Lahadi.
‘Yan sandan Isra’ila sun bude wuta kan wasu da aka zarga da afkawa da mota kan wani shingen binciken ababen hawa a yammacin kogin Jordan, tare da mummunan harbin wata kamar yarinya Bafalasdina dake cikin wata mota dake hannun riga da motar, a cewar ‘yan sanda da jami’an kiwon lafiya.
A jiya Lahadi manyan shugabannin Majalisar Dokokin Amurka suka amince da kasafin kudin da gwamnatin tarayya zata kashe a shekarar 2024 na dala triliyan 1 da digo 6.
Wannan lokacin hutun shine shekara ta biyar da Paul Whelan ya yi a gidan yari na Rasha, inda ake amfani da shi domin cimma namufar siyasar Tarayyar Rasha, da nufin samun galaba a kan Amurka
Gwamnan jihar Filato, Caleb Manasseh Mutfwang, ya shaidawa kotun koli jiya cewa, kotun daukaka kara ba ta yi masa adalci ba wajen soke zabensa.
Wani matashi dan shekara 17 ya bude wuta a wata karamar makarantar sakandare ta Iowa a Amurka, a rana ta farkon komawa makaranta bayan hutun hunturu, inda ya kashe wata yarinya ‘yar aji shida tare da raunata wasu biyar a ranar Alhamis yayin da daliban suka yi shinge a ofisoshi a firgice.
Wani jirgin saman yakin Isra'ila mara matuki ya kai hari kan ofisoshin Hamas da ke yankin Beirut a daren jiya Talata, inda ya kashe babban jami'in Hamas Saleh al-Arouri, kamar yadda kungiyar mayakan da kafar yada labaran Mideast suka bayyana.
A jiya Talata tsohon Shugaban Amurka Donald Trump ya daukaka kara kan hukuncin da sakatariyar harkokin wajen jihar Maine ta jam’iyyar Democrat ta yanke, na haramta masa takara.
An caka wa shugaban jam'iyyar adawa ta Democratic a Koriya ta Kudu wuka a wuya, yayin wata ziyara da ya kai birnin Busan da ke kudancin kasar yau Talata, aka kuma dauke shi a jirgin sama zuwa wani asibitin Jami’a domin yi mashi jinya bisa ga cewar Jami'an jam'iyyar da na kashe gobara.
Fasinjoji 163, 878 ne suka ci gajiyar wannan tallafin sufurin na lokacin bukuwan Kirsimeti da hutun karshen shekara na shugaban kasa a cikin kwanaki 10 na farkon shirin.
Shirin Taskar VOA na wannan makon, shiri ne na musanman da Muryar Amurka ta hada a game da yaki ko tashin hankali da ake fama da shi a Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo, da kuma mawuyacin hali da mutane ke ciki sakamakon rikicin.
Domin Kari