Kungiyar agaji ta SOS Mediterranee a yau Alhamis ta ce, wasu da aka ceto daga wani jirgin ruwan roba da ya barke a tsakiyar tekun Mediterrenean, sun sanar da cewa, wasu mutane 50 da suka tashi daga kasar Libya tare da su mako guda da ya wuce sun halaka a cikin wannan tafiya.