Jamus za ta ba da gudummawar alluran rigakafi 100,000 na cutar kyandar biri wato mpox daga hannun jarin sojojinta don taimakawa wajen shawo kan barkewar cutar a nahiyar Afirka na cikin kankanin lokaci tare da ba da taimako ga kasashen da abin ya shafa, in ji kakakin gwamnati a ranar Litinin.
Akalla mutum 21 da suka hada da kananan yara 11 ne suka mutu sakamakon wani harin da jiragen yaki mara matuka a ranar Lahadin da ta gabata a garin Tinzaouaten da ke arewacin kasar Mali, kusa da inda sojojin kasar suka yi mummunan rauni a watan da ya gabata, in ji 'yan tawayen Abzinawa
Hare-haren 'yan awaren akan ofisoshin 'yan sanda, layin dogo da manyan tituna a Lardin Balochistan da ke Pakistan, tare da daukar fansa da jami'an tsaro suka yi, sun hallak akalla mutane 51, kamar yadda jami'ai suka sanar a ranar Litinin.
Wani matashi a jihar Kaduna ya kirkiro karamin jirgi mara matuki da zai iya gano cututtukan shuka a gonaki; Hukumomi a Kamaru su na gargadin iyaye da su guji karya dokokin hana sa yara aikin karfi; wata kungiya na tara abinci don taimakawa mabukata a Lagos, da wasu rahotanni
Adadin wadanda suka mutu sakamakon hatsarin kwale-kwalen a yammacin Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ya karu zuwa akalla 29 tare da gano akalla mutum 128 da suka tsira da rayukansu, wasu kuma ba a san adadinsu ba, kamar yadda hukumomin yankin suka sanar a ranar Alhamis.
Domin Kari