Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ziyarar Muhammadu Buhari a Maiduguri


Shugaba Buhari a lokacin ziyarar da ya kai Dapchi
Shugaba Buhari a lokacin ziyarar da ya kai Dapchi

Rahotanni da dama sun ce sama da sojoji 100 aka kashe a wannan hari, ko da yake, rundunar sojin kasar ba ta fito ta fadi takamaiman adadin sojojin da ta rasa ba, duk da cewa ta tabbatar da aukuwar harin.

Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari na ziyarar a birnin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya, inda ya je domin halartar taron sojin kasar da ake yi a kowacce shekara.

Ziyarar ta Buhari na zuwa ne, a daidai lokacin da ake ci gaba da jimamin kisan wasu sojin kasar da ake zargin kungiyar Boko Haram da aikatawa a yankin Metele.

Rahotanni da dama sun ce sama da sojoji 100 aka kashe a wannan hari, ko da yake, rundunar sojin kasar ba ta fito ta fadi takamaiman adadin sojojin da ta rasa ba, duk da cewa ta tabbatar da aukuwar harin.

Wakilinmu Haruna Dauda Biu da ke Maiduguri ya ce Buhari ya fara ziyarar ce da kai gaisuwa a fadar Shehun Borno, Abubakar Ibn Umar Garba.

Sannan ya kai ziyarar asibiti domin yin jaje ga sojojin da suka samu raunuka a harin na Metele.

Saurari hirar da Mahmud Lalo ya yi da Haruna Dauda Biu kan ziyarar ta Muhammadu Buhari:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:38 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG