Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Zirga Zirgan Ababan Hawa Sun Koma Yarda Suke A Birnin Khartoum


Mahmoud Dreir
Mahmoud Dreir

Al’ammura sun dawo dai-dai a birnin Khartoum inda aka sake bude shaguna a kasuwanni kuma zirga-zirgar abubuwan hawa ta dawo kan tituna, bayanda kungiyoyin adawa suka kammala tarukkansu na zanga-zanga da yajin kin zuwa wurarensu na aiki.

Nan bada jimawa ba ake sa ran wakilan masu zanga-zangar zasu sake komawa kan teburin tattaunawa da shugabannin gwabnatin mulkin soja ta kasar akan hanyoyin maslaha.

Sojojin dai da ke rike da mulkin kasar tun bayanda suka tumbuke tsohon shugaba Omar al-Bashir a watan Afrilu, sun yarda zasu saki fursunonin siyasa, a cewar jagoran sulhu na musamman daga kasar Habasha Mahmoud Dirir.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG