Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

ZAUREN MATASA: Damina Ta Kankama Amma 'Yan Bindiga Sun Hana Shiga Gonaki Da Ke Nesa Da Gari, Kashi Na 5 - Satumba 4, 2023


Nasiru Adamu
Nasiru Adamu

Zauren matasa ya ci gaba da tattaunawa da matasa a garin Dan Umaru inda matasa da yawa ke noma a karamar hukumar Danko Wasagu dake jihar Kebbi a arewa maso yammacin Najeriya.

Matasa sun taru a zauren inda su ka koka da cewa damina ta kankama amma miyagun iri sun hana shiga gonaki da ke nesa da gari.

Matasan na bukatar dauki daga hukumomi don kar hakan ya zama barazana ga samar da abinci yayin da janye tallafin fetur ya jefa talakawa cikin kuncin rayuwa.
Ra'ayin matasan na nuna ko dai ba za a samu yin noman yadda aka saba ba, to ya kamata mutane su samu damar yin barci da ido biyu rufe.

Saurari shirin cikin sauti:

ZAUREN MATASA: Damina Ta Kankama Amma 'Yan Bindiga Sun Hana Shiga Gonaki Da Ke Nesa Da Gari, Kashi Na 5 - Satumba 4, 2023
please wait

No media source currently available

0:00 0:09:57 0:00

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG