Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Harbe Shanun Makiyaya Kusan 100 a Filato


Shanun makiyaya
Shanun makiyaya

Wasu da ba a tantance ko su wanene ba, sun harbe shanun makiyaya a yankin Kwall, dake karamar hukumar Bassa a jihar Filato, da yammacin ranar Alhamis.

Wannan lamari ya auku ne bayan wani zama na musamman don sasantawa tsakanin al’ummomin yankin don samun dawwamammen zaman lafiya.

Ardon karamar hukumar Bassa, Alhaji Umar Dakare wanda ya shaidawa Muryar Amurka cewa an kashe shanu kusan dari, aka kuma tafi da wadansu, ya yi kiran jama’ar yankin su bar hukumomi su gudanar da bincike.

Shima shugaban matasan kabilar Irigwe, Shinge Dodo Justice, ya ce wasu marasa son zaman lafiya ne ke neman maida musu hannun agogo baya kan zaman lafiyar da suka samu.

Ardon Riyom, Alhaji Mato Ibrahim wanda ya ce shanun mutanensa ne aka kashen, ya jaddada bukatar hukuma ta biyasu diyya don a zauna lafiya.

Domin karin bayani saurari rahotan Zainab Babaji.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:23 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG