Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tawagar Kasashen Renon Faransa Na Nijar Ta Tattara Bayanai Akan Zabuka


Tawagar kasashen renon Faransa a Nijar
Tawagar kasashen renon Faransa a Nijar

Tawagar wadda tana jamhuriyar Nijar ne da nufin tattara bayanai akan zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisar Nijar da zummar gano kurakuran da suka wakana domin a magance na gaba.

Kungiyar tana son tantance irin gudummawar da zata bayar domin inganta zabukan kansiloli da na majalisun karkara da za'a yi a farkon shekarar dubu biyu da goma sha bakwai sun gudana cikin kyakyawan yanayi.

'Yan ba ruwanmu sun ce tawagar tana kasar ne ta duba zaben da aka yi can baya a kasar. Suna san su lalubo bakin zaren yadda za'a gyara kuskuren da aka yi a zabukan baya. Manufar ita ce a tabbatar cewa zabukan gaba sun fi na da kyau.

Mahalarta taron, wasun su sun ce zabukan na baya suna kawai suka tara amma ba inganci ba saboda haka a bar kaza cikin gashinta. Kokari za'a yi a gyara saboda gobe. A gyara kada Nijar ta lalace.

Kungiyar ta sanar cewa zata shirya wani taron karawa juna sani ta hada duka bangarorin siyasa da na fararen hular Nijar a nan gaba kadan domin fadakar dasu akan wasu mahimman dabaru da zasu taimaka wajen kaucewa kurakuran da zasu lalata zabe.

Ga rahoton Souley Barma da karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:23 0:00
Shiga Kai Tsaye

XS
SM
MD
LG