Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Taron Kolin Tarayyar Afirka


Wani jakadan Amurka, mai kula da shiyyar Afirka, Johnnie Carson, ya yi kira da a kara karfin sojoji a Somalia domin samun galaba kan kungiyar al-Shabab.

Wani babban jami’in jakadancin Amurka ya ce ana bukatar Karin sojojin a Somaliya,in da ‘yan gani kashenin Islama, suke yunkurin kifar da gwamnatin riko ta kasar.

Mukaddashin sakataren harkokin wajen Amurka Johnnie Carson,ya yi taro a asirce litinin din nan da shugabannin kasashen Afirka dake gabashi,da kuma arewacin ta, a gefe daya na taron kolin Tarayyar Afirka.
Carson yace Somaliya ta zama kafar fashi a teku da ta’addanci, kuma ta zama dandali da mayakan sakai daga ketare ke zuwa domin ayarsu.

Yace shi da shugabannin kasashen Afirka da ya gana d a su, sun dukufa wajen karfafa rundunar sojoji a Somaliya da nufin murkushe al-Sahab,kungiyar mayakan sakai dake kokarin neman mai da Somaliya kasa mai bin tafarkin tsatstsaurar ra’ayin Islama.

Shugabannin Afirka suna nazarin kara karfin sojojin kiyaye zaman lafiya a Somalia, rundunar da ahalin yanzu take da dakaru dubu shida,galibi daga Uganda da Burundi. Haka kuma Tarayyar tana nazarin karawa rundunar ikon daukar matakan soji kan mayakan sakan kasar.

XS
SM
MD
LG