Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sudan Ta Nemi Amurka Ta Cire Ta a Jerin Kasashe Masu Goyon Bayan Ta'addanci


Bayan da ta kwashe watanni tana fama da rikita-rikitar siyasa, wacce ta yi sanadin hambarar da gwanatin Omar Al-Bashir, gwamnatin wucin gadin kasar Sudan, na neman a cire kasar daga jerin sunayen kasashen da Amurka ta yafa masu rigar masu daukan nauyin ayyukan ta’addanci.

A cewar jami’an gwamnatin kasar, cire sunan Sudan daga jerin sunayen, zai taimaka wa tattalin arzikinta wajen farfadowa, wanda yake fuskantar kalubale tun bayan da aka kawar da Al-Bashir.

A shekarar 1993 Amurka ta saka Sudan a jerin kasashe masu goyon bayan ta’addanci, kan wasu tuhume-tuhume da aka yi wa gwamnatin tsohon Shugaba Al-Bashir na mara baya ga ayyukan na ta’addanci.

Sannan Amurka ta sakawa kasar takunkumi kan zargin goyon bayan kungiyoyin ta’addanci irinsu Al Qaida da Hamas da kuma Hezbollah.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG