Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Mohammadu Buhari A Taron Shawo Kan Dumamar Yanayi A Morocco


Shugaba Mohammadu Buhari
Shugaba Mohammadu Buhari

Shugaba Mohammadu Buhari yayi jawabi a taron kasa da kasa da ake gudanarwa a kasar Morocco domin yin nazari da tsara hayar da za a yaki matsalar dumamar yanayi a Duniya.

A jawabin shugaba Mohammdu Buhari ya nuna irin matakan da Najeriya ke dauka na yaki da matsalolin dumamar yanayi da kuma muhalli, tare da nuna fagen da yake ganin kasashen duniya zasu iya taimakawa Najeriya.

Baban jami’in hulda da jama’a na fadar gwamnatin Najeriya, Mallam Garba Shehu, yace Buhari ya nuna goyon bayan da gwamnatin kasar ke yi kan dakatar da dumamar yanayi wanda illarta ta fito fili. Idan aka duba yawan ruwan da ya rage a tafkin Chadi baifi kashi goma cikin dari na ruwan da ake dashi a baya ba.

Kafewar tafkin Chadi yayi sanadiyar rasa ayyukanyi ga kimanin mutane Miliyan biyar, wadanda ke sana’ar Noma da kamun kifi. Hakan dai ya taka rawa wajen zuwan kungiyar Boko Haram da samun goyon baya a yankin.

Domin karin bayani.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:11 0:00

XS
SM
MD
LG