Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

SARS: Matasa Sun Bukaci a Horas Da ‘Yan Sanda


 Zanga Zangar kin jinin SARS a Jos.
Zanga Zangar kin jinin SARS a Jos.

Ana ci gaba da zanga zangar nuna kin jinin kuntatawa al’umma da jami’an ‘yan sanda suke yi a birane da dama a Najeriya.

Daruruwan matasa a birnin Jos sun fito don gudanar da zanga-zangar fargad da gwamnati ta dauki kwararan matakan ba ‘yan sanda horo ta yadda zasu mutunta jama’a yayin gudanar da aikinsu.

Wadansu da suka gudanar da zanga-zangar sun ce suna bukatar gwamnati tayi wa wadanda jami’an SARS suka ci mutuncinsu adalci, ta kuma ba daukacin ‘yan sandan Najeriya horo da biya musu bukatunsu don su gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

shahararrun-mutane-a-duniya-na-goyon-bayan-kanfen-din-yan-najeriya

yan-najeriya-sun-dage-sai-sun-ga-bayan-rundunar-sars

mun-dauki-matakin-farko-na-yi-wa-rundunar-yan-sanda-garambawul-a-najeriya

Zanga-zangar da tasa matasan toshe babbar hanyar da ta hada jahar Pilato da sauran sassan Najeriya, ta haddasa cunkoso a cikin garin Jos, lamarin da direbobi da fasinjoji suka rika kokawa.

Zanga Zangar kin jinin SARS a Jos
Zanga Zangar kin jinin SARS a Jos

A hirar shi da Muryar Amurka, kwamishinan yada labarai da sadarwa a jahar Pilato, Mr Dan Manjang yace gwamnati zata duba lamarin. Ya kuma yi kira ga matasa su kai zuciya nesa su kuma kiyaye doka da oda yayin gabatar da korafinsu.

Saurari rahoton Zainab Babaji cikin sauti.

SARS: Matasa Sun Bukaci a Horas Da ‘Yan Sanda-3:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:07 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG