Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Salva Kiir Ya Ayyana Dokar Ta-Baci a Wasu Jihohin Sudan ta Kudu


Shugaban Sudan ta Kudu, President Salva Kiir
Shugaban Sudan ta Kudu, President Salva Kiir

Rikicin Sudan ta Kudu da ya ki ci ya ki cinyewa ya kai ga hukumomin kasar sun ayyana dokar ta-baci a wasu jihohi hudu da kabilar Dinka ke rikici a tsakankaninsu, a kasar da ke fama da yakin basasa.

Shugaban Sudan ta Kudu, Salva Kiir ya ayyana dokar ta-baci a jihar da ya fito ta Gogrial da wasu jihohi uku, inda rikici yaki-ci-ya-ki-cinyewa har na tsawon wasu watanni tsakanin mayakan sa-kai na wasu kabilu.

Ministan yada labaran kasar, Michael Makuei, ya ce za a bai wa dakarun kasar karfin ikon tsayar da fadan a jihohin Gogrial da Tonj da Wau da kuma Aweil da suke gabashin Sudan ta Kudu.

Ministan ya fadawa Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters cewa, za a jingine wasu ‘yancin walwalar jama’a yayin kokarin tsayar da wannan fada, sai dai bai yi karin bayani kan wannan ikirarin ba.

Akwai rahotanni dake nuna cewa ana yin artabu a jihar Gogrial tsakanin mayakan sa-kan ‘yan Apuk da kuma Aguok wadanda dukkaninsu ‘yan kabilar Dinka ne.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG