Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Dinkin Duniya Ta Karfafawa Ayyukan Agaji A Morocco Da Libya


Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana bakin cikinsa game da bala'in da ya afku a Libiya da Morocco.

WASHINGTON, D. C. - Da yake magana da manema labarai a ranar Laraba gabanin babban taron Majalisar Dinkin Duniya na mako mai zuwa, Sakatare Janar Guterres ya ce Majalisar Dinkin Duniya na hada kai don tallafawa ayukan agaji a kasashen biyu.

Marrakech, Morocco, 12 Sept. 2023.
Marrakech, Morocco, 12 Sept. 2023.

Hukumomi a kasar Morocco sun sanar a ranar Laraba cewa adadin mutanen da suka mutu sakamakon girgizar kasar ya kai 2,946, yayin da wasu dubbai kuma suka jikkata.

Derna, Libya, Sept.13, 2023.
Derna, Libya, Sept.13, 2023.

A halin da ake ciki kuma, wani rahoto na ranar Laraba na cewa adadin wadanda suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a birnin Derna da ke gabashin kasar Libya ya zarce dubu biyar, kuma ana sa ran adadin ya karu.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG