Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Lauyoyi Mata Sun Jajirce Don Yakar Cin Zarafin Mata Da Yara a Najeriya


Taron Kungiyar Mata Lauyoyi a Jos
Taron Kungiyar Mata Lauyoyi a Jos

Kungiyar mata lauyoyi reshen jahar Pilato ta ce za ta jajirce don ganin an kawo karshen cin zarafin mata da yara a Najeriya.

A wani taron kara wa juna sani na mako guda da kungiyar mata lauyoyin suka shirya a Jos, shugaban kungiyar Mary Izam ta ce yawan rahotannin cin zarafi da suka samu lokacin dokar hana yawo saboda cutar Coronavirus a Jahar Pilato ya sa su damarar yaki da mugayen dabi’un.

Malam Nurudden Usaini Magaji, wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron bitar, ya ce dole sai dukkan masu ruwa da tsaki sun hada hannu don shawo kan wannan lamarin.

Tsohuwar kwamishinan ma’aikatar mata da walwalar jama’a a jahar Pilato, Barista Olivia Dazyem, cewa ta yi kamata yayi a yi garambawul wa dokokin da suka shafi cin zarafin mata da yara.

Domin karin bayani saurari rahotan Zainab Babaji.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:09 0:00


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG