Jama’a Na Tserewa Hare-Haren Da Sojojin Saman Najeriya Ke Kaiwa ‘Yan Boko Haram – 25 Ga Fabrairun 2015
Rundunar sojojin Najeriya sun fidda wani majigin bidiyon da ke nuna yadda suke ratattakar ‘yan kugiyar boko haram da bama-bamai ta sama a arewa maso gabashin kasar da nufin cika kudurin murkushe ‘yan ta’addar. Bidiyon da muryar Amuryar ta samu daga tashar talbijin ta Channels ya nuna yadda mutanen yankin ke ta gudu a gigice a yankin da sojin ke ganin nan ne maboyar ‘yan kungiyar. Kakakin sojojin Najeriya Manjo Janar Chris Olukolade yace an kai harin na sojojin sama a yankunan Gwoza da Bama da kuma dajin Sambisa cikin nasara.
Labarai masu alaka
Zangon shirye-shirye
-
Satumba 13, 2024
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Tabbatar Da Hallaka Halilu Sububu
-
Satumba 03, 2024
Mutum 129 Sun Mutu A Yunkurin Tserewa Daga Gidan Yarin Congo