Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Iran Ta Sanar Da Sake Bude Ofishin Diflomasiyya a Saudiyya


Ministocin harkokin wajen kasashen Iran da China da kuma Saudiyya.
Ministocin harkokin wajen kasashen Iran da China da kuma Saudiyya.

Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta sanar da cewa za ta sake bude ofisoshin diflomasiyya a kasar Saudiyya a cikin wannan mako, tare da maido da huldar diflomasiyya bayan da aka shafe shekaru bakwai ana takaddama a kai, kamar yadda kafar yada labarai ta kasar ta rawaito a ranar Litinin.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Nasser Kanaani ya bayyana cewa, a ranakun Talata da Laraba ne za a bude ofishin jakadancin Iran a Riyadh da karamin ofishin jakadancinta a Jeddah, da kuma ofishin dindindin na kungiyar hadin kan kasashen musulmi.

A watan Maris, Iran da Saudi Arabiya sun amince da kulla huldar diflomasiyya, a wata yarjejeniya da China ta samar, wadda ke wakiltar wani babban ci gaba a yankin.

A shekarar 2016 ne Saudiyya ta katse hulda da Iran bayan da masu zanga-zangar suka mamaye ofisoshin diflomasiyya na Saudiyya a Tehran, da kuma birnin Mashhad da ke arewa maso gabashin kasar a lokacin zanga-zangar da ta haifar da kisan wani fitaccen malamin Shi'a da wasu 46 a masarautar mai arzikin man fetur.

Kanaani ya kara da cewa ofishin jakadancin Iran da ke Riyadh da karamin ofishin jakadancinta a Jeddah, tuni suka fara gudanar da ayyukanta na taimakawa alhazan Iran da ke zuwa Saudiyya domin gudanar da aikin hajji a karshen watan Yuni.

XS
SM
MD
LG