Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka, ta bada sanarwar cewa zata daukaka kara a hukuncin da kotun tarayya ta yanke na hana aiki da wasu muhimman bangarorin dokar dakile ‘yancin bakin hauren da basu da takardun izinin shiga Amurka, a dai dai lokacin da dubban mutane ke ci gaba da zanga-zangar nuna rashin amincewa da aiki da dokar da ta fara aiki a Arizona tun daga jiya Alhamis. Lauyoyin dake baiwa Gwamnar jihar Arizona Jan Brewer kariya, sun shigar da daukaka kararsu a babar kotun daukaka kara dake San Francisco, California. Lauyoyin sun kuma bukaci kotun daukaka karar ta gaggauta yanke hukunci.Yayin da ake wannan, ’yan sanda a Phoenix sun kama mutane sama da talatin saboda toshe titunan da ake bi a zanga-zangar da suka shirya a wajen ofishin shugaban ‘yan sanda jiya Alhamis.Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka, ta bada sanarwar cewa zata daukaka kara a hukuncin da kotun tarayya ta yanke na hana aiki da wasu muhimman bangarorin dokar dakile ‘yancin bakin hauren da basu da takardun izinin shiga Amurka, a dai dai lokacin da dubban mutane ke ci gaba da zanga-zangar nuna rashin amincewa da aiki da dokar da ta fara aiki a Arizona tun daga jiya Alhamis. Lauyoyin dake baiwa Gwamnar jihar Arizona Jan Brewer kariya, sun shigar da daukaka kararsu a babar kotun daukaka kara dake San Francisco, California. Lauyoyin sun kuma bukaci kotun daukaka karar ta gaggauta yanke hukunci.Yayin da ake wannan, ’yan sanda a Phoenix sun kama mutane sama da talatin saboda toshe titunan da ake bi a zanga-zangar da suka shirya a wajen ofishin shugaban ‘yan sanda jiya Alhamis.
Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka tace zata daukaka kara a kan hukuncin kotun tarayya dangane da dokar da zata bada damar dakile ‘yancin bakin haure
![In this June 15, 2010 file photo, Arizona Gov. Jan Brewer speaks in Phoenix. With the scrawl of a pen, Brewer awakened a dormant, but politically explosive issue of illegal immigration, sending shock waves across the political spectrum in an election year](https://gdb.voanews.com/f4f87319-83b5-4dfc-94c5-a66c4faacc1b_w250_r1_s.jpg)
Gwamnatin jihar Arizona dake Amurka, ta bada sanarwar cewa zata daukaka kara a hukuncin da kotun tarayya ta yanke na hana aiki da wasu muhimman bangarorin dokar dakile ‘yancin bakin hauren.