Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Guinea Bissau, Ivory Coast Za Su Bude Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka


'Yan wasan Ivory Coast masu masaukin baki suna atisaye
'Yan wasan Ivory Coast masu masaukin baki suna atisaye

A rukunin A, akwai Najeriya, Ivory Coast, Guinea Bissau da kuma Equatorial Guinea.

‘Yan wasan Guinea Bissau za su kara da masu masaukin baki Ivory Coast a wasan farko da zai bude gasar cin kofin nahiyar Afirka.

Kasar ta Guinea-Bissau ta shawo kan matsalolinta a fagen kwallon kafa inda mafi akasarin ‘yan wasanta wadanda suke taka leda ne a nahiyar turai kuma ta halarci gasar ta sau hudu a jera a baya-bayan nan.

Guinea- Bissau na daga cikin kasashen Afirka da ba su taba lashe kofin gasar ba, amma kocinta Baciro Cande, ya ce yana da kwarin gwiwa za su kai ga gaci.

Kasar na rukunin A, wanda ke dauke da Najeriya, Ivory Coast da kuma Equatorial Guinea.

Wasan na yau za a kara ne a filin wasa na Alassane Ouattara da ke Abidjan, babban kasar kasar ta Ivory Coast.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG