Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gobe Alhamis Nigeria ke shirin maido da zirga-zirgar jiragen kasa daga Ikko zuwa Ilori


Tashar jiragen kasan Nigeria dake birnin Ikko ke nan inda jami'an hukumar zirga-zirgar jiragen kasa ke fatan kashe kudi Dala miliyan 166 domin ayyukan sake farfado da ayyukan zirga-zairgar jiragen kasa a Nigeria.
Tashar jiragen kasan Nigeria dake birnin Ikko ke nan inda jami'an hukumar zirga-zirgar jiragen kasa ke fatan kashe kudi Dala miliyan 166 domin ayyukan sake farfado da ayyukan zirga-zairgar jiragen kasa a Nigeria.

A ran Alhamis ce hukumomin Zirga-Zirgar jiragen kasa a Nigeria, wato “Railways”, zasu maido da Zirga-Zirga da jigilar Fasinja tsakanin tashoshin Ikko zuwa Ilori jihar Kwara.

A rahoton da wakilin Muryar Amurka(VOA) Ladan Ibrahim Ayawa ya aikowa sashen Hausa na cewa , hakan ba shine karon farko da hukumar “Railway” ta Nigeria ta fara wnanan shirin ban a gyaran ayyukan zirga-zirgar jiragen kasa.

A watan Maris, wato watan Ukun farkon wannan shekarar, jirgin kasa dauke da fasinja ya tashi daga tashar Ikko zuwa Ibadan, shalkwatar jihar Oyon Nigeria, duka a cikin shirin maido da zirga-zirgar daki-daki. Ran Alhamis ake shirin gudanar da mataki na biyu, sannan makatki na uku sine wanda zai taso daga Ikko zuwa Kano. Idan ba’a manta ba, tun watan Satumban day a gabata ne Gwamnatin Tarayyar Nigeria ta sayo sabbin kan tukwanen jiragen kasa guda 25 kuma an rarrabasu duk zuwa sauran tashoshin jiragen kasa a Nigeria.

XS
SM
MD
LG