A bayan hare-haren da suka kashe mutane akalla 127, wadanda kungiyar ISI ta ce ita ce ta kai, Faransawa su na ci gaba da jimami yayin da shugabanninsu ke lasar takobin cewa wadanda suka kai zasu ga tashin hankali.
Faransawa Na Ci Gaba Da Jimamin Wadanda Suka Mutu Ko Suka Ji rauni
A bayan hare-haren da suka kashe mutane akalla 127, wadanda kungiyar ISI ta ce ita ce ta kai, Faransawa su na ci gaba da jimami yayin da shugabanninsu ke lasar takobin cewa wadanda suka kai zasu ga tashin hankali.

5
Shugaba Francois Hollande yana jawabi ga al'ummar Faransa a bayan hare-haren ta'addancin da kungiyar ISI ta ce ita ce ta kai a daren jumma'a 13 Nuwamba, 2015. Shugaban ya ce duk mai hannu a wadannan hare-haren zai gwammace kida da rawa.

6
Wani mutumi ya rike kai a lokacin da yake ajiye furanni na jimami a kofar wani gidan abinci mai suna Carillon cafe, a Paris, Nov.14, 2015.

7
Taswirar wuraren da aka kai ma hare-hare a birnin Paris.

8
Wasu 'yan jarida su na aiki a kofar wani gidan abinci inda ake iya ganin yadda harsashi ya huda gilashin kofar a Paris.