Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ethiopia Ta Zargi Masar Da Zuga 'Yan Tawayen Kasarta


Gwamnatin Ethiopia tana zargin Masar da iza yan tawayen kasar, wanda hakan ya tilastawa Ethiopian ta kafa dokar ta baci a shekaranjiya Lahadi.

Ethiopia tace tana da shaida mai yawa dake tabbatar da ana horar da yan tawayen, ana basu tallafin kudi a Masar, inji kakakin gwamnatin Ethiopia, Getachew Reda a hirarsa da manema labara a jiya Litinin.

Tun cikin makon jiya dai kasar Masar take ta musunta bada wani taimako ga ‘yan tawayen na Ethiopia.

Masar da Ethiopia sun dade suna samun rikici tsakaninsu a kan atun mallakar ruwan kogin Nilu, inda Masar ke cewa madatsar ruwan da Ethiopia ke ginawa a kogin zai rage yawan ruwan da Misra din ke samu.

Getachew yace dokar ta bacin watanni shidan da aka kafa zata baiwa gwamnati daman daukan kwararan matakai a kan kungiyar OLF da ta shirya tarukan zanga zanga a duk fadin jihar Oromia a makon da ya gabata.

Kungiyoyin kare hakkin Bil Adama da jami’an ‘yan adawa sunce mutane akalla 400 ne aka kashe a wannan zanga zanga ta kin jinin gwmanti a shekara da ta gabata.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG