Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Da Alama Karin Haraji Akan Tama Da Karafa Ba Zai Shafi Wasu Kasashe Ba


Sarah Sanders sakatariyar watsa labaran Fadar White House wadda ta ce karin harajin ba zai shafi wasu kasashe ba
Sarah Sanders sakatariyar watsa labaran Fadar White House wadda ta ce karin harajin ba zai shafi wasu kasashe ba

Da alama cewa karin haraji kan tama da karafa da shugaba Trump ya lashi takobin yi ba zai shafi kasashen Canada da Mexico ba, kasashe biyu dake makwaftaka da Amurka kamar yadda Sarah Sanders ta sanar jiya Laraba

Akwai alamun cewa za a cire wasu kasashen daga cikin shirin karin kudin fito da shugaba Donald Trump na Amurka ke dab da sanarwa a kan wasu karafa da ake shigowa da su Amurka daga waje.

Sakatariyar watsa labarai ta fadar White House Sarah Huckabee Sanders ta shaidawa manema labarai a ranar Talata cewa, “muna sa ran shugaban kasa zai sa hannu a kan wani abu karshen mako, kuma mai yiwuwa ba zai shafi kasashen Mexico da Canada ba bisa dalilan tsaron kasa, kuma akwai yiwuwar cewa za a tsame wadansu kasashen ma a bisa irin wannan dalili."

Majiyoyi a fadar White House sun kuma ce mai yiwuwa a fito da wannan sabon shirin karin kudin fito na shugaba Trump da ake cacar baki sosai a kai a lokacin wani bukin sanya hannu da karfe 3:30 na rana, watau 9:30 na dare agogon Najeriya yau alhamis a fadar White House.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambaci ta bakin wani babban jami’in Amurka yana cewa, za a fara aiwatar da matakin kimanin makonni biyu bayan shugaba Trump ya sa hannu a kai.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG