Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cinikin Dabbobi Ya Yi ‘Kasa a Nijar Gabannin Babbar Sallah


Kasuwar dabbobi a jamhuriyar Nijar
Kasuwar dabbobi a jamhuriyar Nijar

Ya yin da al’umar musulmi ke shirin gudanar da shagulgulan babbar sallah, kasuwannin dabobi a birnin Yamai na jamhuriyar na fama da rashin ciniki.

Da alamu matsalar tsaron da ake fuskanta a kasar Mali, ita ce ta hana mutane shigowa da dabbobinsu domin cin kasuwar sallah a jamhuriyar Nijar.

Ya yin da ya rage saura mako guda ayi babbar sallah, wakilin Muryar Amurka, Sule Muminu Barma, ya ziyarci kasuwar dabbobi ta Turaku, ya fuskanci rashin hada-hadar kasuwanci irin wadda aka saba yi a baya.

Halin ‘karancin abincin dabobi da aka yi fama da shi a bana, ya haifar da matsalar karancin dabobi a kasuwanni inji Abdullahi Yahahai, mai sana’ar sayar da dabbobi.

Shiga da fice tsakanin Mali da Nijar sun ragu matuka, sanadiyar tashe-tashen hankulan da ake fuskanta a arewacin Mali, lamarin da ya haddasa tsoro a zukatan mutane musammanma ‘yan kasuwa dake harkokinsu a kasashen biyu.

Matsin tattalin arzikin da kasar Nijar ke fama da shi a halin yanzu, ya jefa magidanta da dama cikin ‘kangin fatara lamarin da ya sa wasu daga cikinsu ke ganin samun abin yanka a bana sai yadda hali ya yi.

Domin karin bayani saurari rahotan Sule Muminu Barma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:05 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG