Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sami Asarar Rayuka Bayan Nutsewar Wani Jirgin Ruwa a Congo


Hukumomi a gabashin Congo sun ce akalla mutane talatin sun mutu kana wasu mutane dari biyu sun bata bayan wani jirgin ruwa ya nutse a wani tafki.

Kantomar yankin Inongo, Simon Mboo Wemba, ya fadawa kamfanin dillancin labaran Associated Press cewa da yammacin jiya Lahadi cewa galibin mutane da suka cikin jirgin ruwan da ya niste a tafkin Mai-Ndombe malamai ne.

Kantomar yace sun yi amfanin da jirgin ruwa ne zuwa karba albashin su ne saboda lalacewar hanyoyin yankin.

Sai dai nan da nan ba a iya gano adadin mutane dake cikin ruwan ba yayin da jirgin ya fada cikin yanayi mara kyau da yammacin ranar Asabar.

Amma jami’ai sun kiyasta akwai daruruwar mutane a cikin jirgin. Sama da mutane tamanin sun kubuta.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG