Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An komo da wata mace ‘yar Jihar Texas wadda ta gudu zuwa Najeriya a bayan da gobara ta tashi a gidan ta ke renon yara, har wasu yara 4 suka mutu


Jessica Tata
Jessica Tata

An komo da wata mace ‘yar Jihar Texas wadda ta gudu zuwa Najeriya a bayan da gobara ta tashi a gidan ta ke renon yara, har wasu yara 4 suka mutu. A ranar asabar An komo da wata mace ‘yar Jihar Texas wadda ta gudu zuwa Najeriya a bayan da gobara ta tashi a gidan ta ke renon yara, har wasu yara 4 suka mutu.

An komo da wata mace ‘yar Jihar Texas wadda ta gudu zuwa Najeriya a bayan da gobara ta tashi a gidan ta ke renon yara, har wasu yara 4 suka mutu. A ranar asabar An komo da wata mace ‘yar Jihar Texas wadda ta gudu zuwa Najeriya a bayan da gobara ta tashi a gidan ta ke renon yara, har wasu yara 4 suka mutu. A ranar asabar hukumar ‘yan sanda ta kasa da kasa, Interpol, da jami’an ma’aikatar harkokin wajen Amurka suka kama Jessica Tata a garin fatakwal a kudancin Najeriya.hukumar ‘yan sanda ta kasa da kasa, Interpol, da jami’an ma’aikatar harkokin wajen Amurka suka kama Jessica Tata a garin fatakwal a kudancin Najeriya. A yanzu dai ana tsare da ita a wani gidan kurkuku a Jihar Texas. Ba a bayar da belinta ba. Jessica Tata tana fuskantar tuhume-tuhume 14, cikinsu har da haddasa mutuwa da kuma gudu daga kasa domin kada ta fuskanci shari’a. Masu gabatar da kararraki sun yi zargin cewa Tata ta bar wasu yara 7 da aka ba ta reno a cikin gida, ta fita yin saye-saye a kanti. Man girki da ta dora a kan wuta ta manta da shi, ya kama da wuta, ya kuma kama wannan wurin da take renon yaran har hudu suka mutu, uku kum asuka ji mummunan rauni. Kwana biyu bayan abkuwar wannan al’amari, Tata ta gudu zuwa Najeriya inda ‘yan’uwanta suke. Hukumomi a nan Amurka sun sanya ta a cikin jerin mutane 15 da suka fi nema ruwa a jallo.

XS
SM
MD
LG