WASHINGTON, D. C. - Ma’aikatar ba ta bayyana takamaimen wadanda ke da hannu a fadan ba, ko kuma tsawon lokacin da aka yi ba, amma a kullum yankin na ganin fadace-fadacen da ake yi tsakanin manoma da makiyaya, ko kuma wasu kungiyoyi, dangane da filaye.
A wata sanarwa da gwamnatin kasar ta fitar ta ce a sakamakon fadan an kama mutane 175 a wurin, inda wasu ‘yan bindiga suka kona wani bangare mai yawa na kauyen Tileguey da ke lardin Ouaddai.
Ministan tsaron jama'a Janar Mahamat Charfadine Margui ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP a cikin wani sakon wayar tarho cewa "An shawo kan lamarin amma ana kokarin sasanta bangarorin daban-daban."
Ministan ya kasance a wurin da aka gwabza fadan, inda ya jagoranci tawagar gwamnati da sojoji da nufin ba da cikakken haske kan lamarin.
A gabashi da kudancin Chadi, inda mazauna yankin da dama ke dauke da makamai, ana ta samun rikici ne a yayin da manoma ke zargin makiyaya da barin dabbobi su yi kiwo a gonakinsu ko kuma su tattake amfanin gona.
-AFP
Dandalin Mu Tattauna