Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fatattaki 'Yan ISIS Daga Wani Muhimmin Wuri A Syria


Wata kungiyar rajin kare hakkin bil adama a Syria ta ce, dakarun Syria masu samun goyon bayan Amurka, sun kwato wani muhimmin gari, wanda daya ne daga cikin wasu yankunan kasar Syria da su ka rage a hannun ISIS.

Kungiyar ta kula da hakkin bil adama a Syria ta ce “bayan wani mummunan fada na tsawon mako guda da ya hada da hare-haren jiragen sama, Dakarun rajin tabbatar da dimokaradiyya a Syria (SDF, a takaice), sun yi nasarar fatattakar kungiyar ISIS daga Hajin." Hajin dai, na lardin Deir Ezzor ne, mai tazarar kilomita 30 daga kan iyakar Syria da Iraki.

Mayaka wajen 17 na gamayyar Kurdawa da Larabawa da kuma dakarun SDF sun hada hannu wajen fatattakar 'yan ISIS daga yankin da ya rage a hannunsu a Syria, a cewar Abdel Rahman, shugaban kungiyar ta rajin kare hakkin dan adam a Syria.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG