Bernie Sanders, da ke neman tikitin takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar Democrat, ya yi kira ga magoya bayansa da su hada kai domin tunkarar zaben da ke tafe a wannan shekara.
Sanders shi ya lashe zaben sharar fage da aka yi a jihar Nevada da ke yammacin Amurka a karshen makon da ya gabata.
Wannan nasara ta Sanders wacce ta ba shi damar zama dan takara na gaba-gaba da ya samu yawan wakilai ko delegate – ta kara dabbaka matsayinsa na dan takarar da ake ganin ya fi fice cikin jerin masu neman tikitin kara wa da Shugaba Donald Trump.
“Idan muka zama tsintsiya-madaurinki- daya, ba Trump kadai za mu kayar ba, za mu samu damar sauya fasalin kasar nan, mu kuma kafa gwamnati da tattalin arzikin da zai amfani kowa da kowa.” Sanders ya ce.
Kamar yadda manyan kafafen yada labaran Amurka suka bayyana, Sanders ya samu kashi 44 cikin 100 daga mazabu 11 da ke jihar ta Nevada.
Sai tsohon mataimakin shugaban kasa Joe Biden wanda ya samu kashi 25, sai kuma tsohon Magajin Gari Pete Buttigieg wanda ya samu kashi 15.
Wannan zabe na sharar fage, shi ne na uku a zabukan da za su kai ga na fidda gwani, daga cikin ‘yan takarar da ke neman tikitin jam’iyyar ta Democrat.
A baya an yi makamancinsa a jihohin Iowa da kuma New Hampshire.
Nan gaba ana sa ran yin wani zaben a jihar South Carolina, kafin nan a dangana da babban zaben fidda gwani.
Shi dai Trump, ya sha ayyana cewa dukkan ‘yan takarar na jam’iyyar ta Democrat ba za su iya kara wa da shi ba domin "duk suna da rauni."