Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Na Zargin Saudi Arebiya Da Sace Dan-Jarida Khashoggi


Wasu 'yan rajin kare hakkin bil'adama na neman a sako dan jaridar da aka sace.
Wasu 'yan rajin kare hakkin bil'adama na neman a sako dan jaridar da aka sace.

Kasar Amurka na cigaba da zargin kasar Saudi Arebiya da daukewa ko boye dan jaridar nan Khashoggi.

Shugaba Donald Trump na Amurka yace yanzu haka wasu jami’an Amurka din na kasar Turkey, suna kokarin gano abinda ya faru ga wani hamshakin dan jarida Ba’amurke, Jamal Khashoggi, wanda ganin karshen da aka yi mishi shine lokacinda yake shiga karamin ofishin jakadancin Saudi Arebiya dake birnin Santanbul, kuma daga sannan ba’a sake jin duriyarsa ba.

Trump yace, “an gan shi ya shiga ginin, amma ba’a ga fitowarsa ba, wanda wannan ke nuna alamar kamar baya doron kasa ke nan.”

Hukumomin kasar Turkiyya sunyi imanin cewa Mr. Khashoggi, wanda gogaggen dan jarida ne, mai yawan rubutawa jaridar Washington Post sharhi, kuma yayi kaurin suna wajen yawan sukar lamirin Yariman Saudiyya Mohammed Salman, ya rasa ransa ne a hannun wasu mutane 15 da gwamnatin ta turo musamman zuwa Santanbul don ganin bayansa.

Zargin da hukumomin Saudiyya suka bayyana da cewa “ba ya da hujja ko kadan.” A wani rahoton da ta buga a baya-bayan nan, jaridar ta Washington Post, tace wasu bayanai da hukumomin leken assiri na Amurka suka samu, na nuna shirin da shi Yarima Salman yayi nasa a kamo dan jaridar, a maida shi Saudi Arebiya ta jirgin sama don a tsare shi.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG