Kafafen yada labaran kasar ta Korea ta Kudu sun ce an dan samu jinkirin kwana biyu da farawa, bayan da aka samu wani sojan kasar da cutar coronavirus.
A ranar Lahadi gamayyar hafsoshin sojin kasar suka ce cutar ta COVID-19 ce ta sa aka jinkirta atisayen.
A baya an tsara za a fara shi ne a yau Lahadi, amma kuma aka dage zuwa Talata bayan da gwaji ya nuna wani sojan kasar ta Korea ta Kudu ya kamu da cutar a ranar Juma’a, wanda asali aka tsara zai shiga atisayen, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Yonhap ya ruwaito.
Korea ta Arewa dai ta kan sa ido kan wannan atisayen hadin gwiwa na shekara-shekara, wanda take kallon sa a matsayin “atisayen shirin kaddamar da yaki.”
A ‘yan shekarun bayan nan, an rage gudanar da shi, a wani mataki na kokarin ganin an cimma matsaya a tattaunawar da ake yi na a kwance shirin da hukumomin Pyongyang ke yi na kara makamin nukiliya.
Facebook Forum