Dokar kasar Amurka ta ba ‘yan ci rani da ke da izinin zama ‘yan kasa ‘yancin zabe da kuma tsayawa takara kamar sauran Amurkawa. Damar da mutane da dama su ke dauka da muhimmanci
A yayin da kasashen duniya suka maida hankali kan kasar Amurka don ganin yadda zaben kasar ke gudana a gefe guda kuma masharhanta na ci gaba da yin sharhi, sun ce zaben ma’auni ne kan yadda tattalin arzikin duniya da kuma zaman lafiya zasu kasance.
Da sanyin safiyar yau Talata masu kada kuri’a zasu fita zuwa runfunan zabe don zabar gwaninsu inda zasu jure layi mai tsawo don ganin sun yi amfani da ‘yancin da dokar kasa ta basu na zabar wanda zai shugabance su.
A yau 3 ga watan Nuwamba, masu kada kuri’a a New Jersey, zasu yanke hukunci kan ko a halatta amfani da tabar Wiwi a hukumance.
A ranar jajiberin zaben Shugaban kasa a Amurka masana harkokin siyasa a Nigeria sun ci gaba da yin sharhi kan babban zaben da za a yi ranar Talata 3 ga watan Nuwamba.
Shugaban Amurka Donald Trump da abokin kaeawarsa na jam'iyyar Democrat, tsohon mataimakin shugaban kasa Joe Biden, sun ziyarci jihohin da ake yiwa lakabi da fagen daga jiya Lahadi, don karawa magoya bayansu karfin gwiwa.
Yayin da Amurka ke shrine gudanar da zabuka ciki har da shugaba kasa wasu Amurkawa 'yan asalin Afirka su ma sun tsaya neman takara a matakai daban-daban.
Shugaban Amurka Donald Trump ya fadawa manema labarai a jiya Laraba cewa kuru’un da yake samu a jihohin da ake kira da filin daga sun haura manyan binciken jin ra’ayi dake nuna tsohon mataimakin shugaban kasa Joe Biden na kasa shi.
Yakin neman zabe na kara zafafa, a daidai lokacin da ake makon karshe kamun babban zaben.
Alkaluma Jami’ar Johns Hopkins dake kididdigar masu dauke da cutar coronavirus na nuni da cewa Amurka ta zarra da adadin wadanda suka kamu da coronavirus mutum miliyan 9 a juma’ar nan, inda aka samu sababbin kamuwa miliyan 1 a cikin makonni biyu.
Manyan 'yan takarar shugabanci kasar Amurka Donald Trump na Jam'iyar Republican da abokin karawarsa Joe Biden sun dukufa wajen sukar juna musamman game da annobar coronavirus gabannin zaben na 3 ga watan Nuwamba.
Shugaban Amurka Donald Trump da ke takara karkashin jam’iyyar Republican, ya kada kuri’arsa a Florida a zaben shugaban kasa da za a yi na ranar uku ga watan Nuwamba.
Domin Kari