Gwamnan na Jihar Jigawa yana maida martani ne ga wata takardar da jami'in yada labaran kyamfe na Buhari, Malam Garba Shehu, ya rubuta cewa Sule Lamido da wasu su na shirin kaddamar da wai gangamin yin batunci ga Janar Muhammadu Buhari domin bakanta shi a idanun 'yan Najeriya.
Labaran Zaben 2015 Daga Ibrahim Alfa Ahmed
Shugaban hukumar zabe ta INEC, yace zai nazarci hukumcin da wata kotu a Lagos ta bayar cewa kada gwamnati ta yi amfani da sojoji a rumfunan zabe a duk fadin kasar ranar zabe.