Bayan fashewar tagwayen boma-bomai a tashar motar Nyanya dake birnin tarayyar Abuja, hukumomi sunce an rasa rayuka sama da mutum 71, da kuma sama da 100 wadanda suka jikkata. Wasu da suka rayu na bukatar tallafin jinni, shiyasa likitocin asibitocin da aka kai masu jinya suke kira ga jama'a su bada tallafin jini.