Hare haren ta’addanci da tada boma bomai a guraren ibada, makarantu, kasuwanni da tashoshin mota harma da bankuna da gidajen mutane a arewacin Najeriya, alamune dake nuna gazawar gwamnatin kasa a bangaren tsaro, saboda haka ya zama dole al’umma su kare kansu domin gwamnati ta kasa samar musu da kariya, acewar Sheikh Dahiru Bauci.