Birtaniya na shirye-shiryen nadin sarautar Sarki Charles III, wanda zai gudana a ranar Asabar. An gayyato shugabannin duniya da dama da shugabannin kasashe zuwa wannan taron mai dimbin tarihi, yayin da ake sa ran miliyoyin mutane za su kalla ta talabijin.
A shekara ta biyu jere, kasar Ghana ta sake faduwa a kididdigar ‘yancin ‘yan jarida ta shekara-shekara da kungiyar Reporters without Borders (RSF) ta fitar a ranar Laraba, ranar ‘yancin ‘yan jarida ta duniya.
Mutumin wanda aka bayyana sunansa a matsayin Francisco Oropeza mai shekaru 38 ya tsere bayan da ya harbe mutanen a garin Cleveland mai tazarar kilomita 72 daga Houston babban birnin jihar ta Texas.
Dakarun Sudan sun ce Amurka da Saudiyya ne suka shiga tsakani aka cimma wannan matsaya ta tsagaita bude wuta wacce ta fara aiki da tsakar daren Litinin.
India, wacce ta gudanar da kidayar jama’a ta karshe a shekarar 2011, ba ta ce uffan ba kan wannan hasashe da Majalisar Dinkin Duniya ta yi.
A Nuwamban bara, Kungiyar ta EEA ta bada sanarwar cewa mutane dubu biyu da talatin da takwas ne suka mutu da kananan shekaru a shekara ta 2020 a Tarayyar Turai da ya hada da kasar Iceland, Leichtenstein, Norway, Switzerland da Turkiyya.
A ranar Asabar an yi ta barin wuta yayin da jiragen yaki ke tashawagi a sararin samaniyar Khartoum a cewar shaidu.
Jami’an Majalisar Dinkin Duniya sun ce matsalar yunwa na ci gaba da karuwa a yankin Yammacin nahiyar Afirka.
Ma'aikatar harkokin wajen Nijar ta tabbatar da labarin kama wasu ' yan kasar a Saudiya dake dauke da miyagun kwayoyi. Sai dai kawo yanzu ba a yanke musu hukunci ba kuma ba a san makomar su ba a cewar hukumomi.
Zababben shugaban Najeriya, Bola Tinubu, da Dokta Ngozi Okonjo-Iweala, babbar darakta a Cibiyar kasuwanci ta duniya, sun shiga jerin mutane 100 da suka fi tasiri a duniya na shekarar 2023 da Mujallar Time ta fitar.
Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Litinin zai bar Ministan Tsaro Yoav Gallant a mukaminsa bisa la’akari da yadda matsalar tsaro ke kara ta’azzara, yana mai sauya matakin korar ministan da ta janyo zanga -zanga tare da tayar da hankula a kasashen waje.
A jawabin sakon Ista da ya karfafa batun bege, ranar Lahadi Fafaroma Francis ya yi addu'o'i ga al'ummar Ukraine da Rasha, ya kuma yaba wa kasashen da suka karbi 'yan gudun hijira.
Domin Kari