An ruwaito takardar bayan taron da kungiyar gwamnonin ta fitar na cewa, “gwamnonin sun amince su cigaba da tattaunawa da muhimman masu ruwa da tsaki domin samun matsayar da dukkanin bangarorin zasu amince da ita.”
A yau Alhamis aka bayyana hakan, a yayin da Shugaban Majalisar Dattawan, Godswill Akpabio ya jagoranci zamanta bayan dawowa daga hutu domin cigaba da sabon zango a ayyukan majalisar.
Hukumomin Najeriya sun ayyana dokar ta-baci a kasar tare da kaddamar da matakan dakile yaduwar cutar amai da gudawa da ake kira kwalara, wadda ta hallaka mutane sama da 50.
Da safiyar Laraban nan ne aka wayi gari da samun tashin gobara a matatar man fetur ta Dangote a jihar Legas da ke kudu maso yammacin Najeriya.
A yau laraba ne El-Rufa'i ya maka Majalisar Dokokin Kadunan a gaban babbar kotun tarayya dake jihar akan tauye masa hakkokinsa.
Sanarwar da mai magana da yawun majalisar kuma shugaban kwamitinta akan harkokin yada labarai da hulda da jama'a, Akin Rotimi, ya fitar a yau Talata tace, yayin ganawar da misalin karfe 1 na rana, rashin lafiya ta rufe jami'in.
Ministan Yada Labarai da wayar da kan al'umma, Muhammad Idris, ne ya bayyana hakan a yau Talata yayin da yake zantawa da manema labaran fadar gwamnatin game da shawarwarin da aka cimma yayin zaman majalisar.
Kusan gidajen mai 2,000 ne aka rufe a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya domin nuna adawa da shirin yaki da fasa kwaurin da hukumomi ke yi wa wasu dillalan man fetur.
Gwamnan jihar Nasarawa Abdullahi Sule, ya bayyana wa Muryar Amurka cewa gwamnonin sun kafa kwamiti da zai yi duba kan mafi ƙarancin albashi da jihohi zasu iya biya, kuma ya ce a shirye yake da yayi na’am da rahoton kwamitin.
Wata Sanarwa dauke da sa hannun hadimin gwamnan jihar Sokoto akan harkokin yada labarai, Abubakar Bawa, ya musanta zargin ya kuma ce hakan na neman kawo cikas ga alakar da ke tsakanin gwamnatin jihar da fadar Sarkin Musulmi.
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe Mataimakin Shugaban Jami’ar Usman Danfodio da ke Sakkwato, Farfesa Yusuf Saidu.
Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a yau Alhamis yayin taron kolin zaman lafiya da tsaro a shiyar arewa maso yammacin Najeriya daya gudana a jihar Katsina.
Domin Kari