Babbar Kotun Jihar Legas ta umarci tsohuwar Ministar Jinkai da walwalar jama’a Sadiya Umar Faruk, ta bayyana yadda ma’aikatar ta, ta kashe Naira Biliyan 729 karkashin kulawar ta, bayan da kungiyar kare 'yancin 'yan kasa da kididdigar ayyuka ta SERAP ta shigar da ita kara.