Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Neja, Janar Abdullahi Bello Muhammad Mai ritaya, yace har yanzu basu tantance yawan 'yan bindigar da aka hallaka ba amma zuwa nan gaba zasu kammala bincike.
Majalisar Wakilai ta yi kira ga Gwamnatin Tarraiya da ta dakatar da Shugaban Hukumar Kula da harkar man fetur ta Najeriya har sai an kammala binciken zarge-zargen da ake yi wa abinda ta kira "kalamai mara dadi da zai iya kashe wa kasar kasuwa" da shugaban hukumar ya yi.
Zanga-zangar tsadar rayuwa da aka shirya gudanarwa a watan Agusta na kara daukar hankali a shafukan sada zumunta.
A yayin da hauhawar farashi ke kara tsananta, babban bankin Najeriya wato CBN ya sake kara kudin ruwa da maki 50, daga kaso 26 da digo 25 zuwa kaso 26 da digo 75 cikin dari lamarin da wasu ‘yan kasa ke ganin cewa yana kara tsananta tsadar kayayyakin abinci.
A sakon daya wallafa a shafinsa na X a yau Talata, Kyari, ya bukaci shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya fito fili ya bayyana sunan jami’in NNPC daya mallaki masana’antar tace albarkatun man fetur a kasar Malta.
Majalisar ta amince da dokar ne ranar Talata bayan da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya aika kudirin doka kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa zuwa Majalisar domin amincewa da shi.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya aika kudirin doka kan sabon mafi karancin albashin ma’aikata na kasa zuwa majalisar dokokin kasar domin amincewa da shi.
Mabiya Addinin Kirista Iklisiyyar United Methodist Church a Najeriya, sun gudanar da zanga zanga ta lumana don nuna kyama ga batun auren jinsi da wassu Shugabannin Iklisiyar Methodist Church ke kokarin ganin mabiyan sun amince dashi.
Kwararru a fannin siyasa da gudanar da mulki a Najeriya sun bayyana ra'ayoyi mabanbanta kan janyewa daga tsayawa takara da shugaba Joe Biden ya yi, inda wasu ke gani ya yi abin da wasu kasashe za su yi koyi da shi.
Kotun Daukaka Kara dake zamanta a Legas ta tabbatar da hukuncin kisa akan wani dan asalin denmark, Peter Nielsen, wanda aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2022 saboda hallaka matarsa ‘yar Najeriya, Zainab da diyarsu, Petra.
A yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce a game da ingancin man dizal da matatar man Dangote ke fitarwa inda wasu ke ganin akwai masu son ganin bayan kamfanin, hukumar kula da dokokin fannin man fetur ta NMDPRA ta sake jaddada cewa ba haka abin ya ke ba.
Domin Kari