Dubban magoya bayan babbar jam’iyyar adawa ta NDC ne suka hallara a filin wasa na Zurak da ke unguwar Madina, a Accra babban birnin Ghana, domin gangamin karshe na jam'iyyar, a wani yunkuri kafin babban zaben da za a gudanar gobe Asabar, 7 ga watan Disamba