Hukumar wanzar da zaman lafiya da sulhu a Jihar Filato ta yi kira ga daukacin al'umma da su hada kai da masu ruwa da tsaki domin samar da zaman lafiya mai dorewa.
Al’umomin Fulani da na Birom dake karamar humar Barikin Ladi a jihar Filato, sun bukaci hukumomin tsaro da su dukufa wajen gudanar da aikinsu na tsaron lafiyar jama’a da dukiyoyinsu.
Al'ummar Jihar Filato sun bayyana ra'ayinsu game da hukuncin da kotu ta yankewa tsohon Gwamna Jihar Joshua Dariye.
Rundunar 'yan sanda jihar Filato ta bayyana damuwa kan yawaitar fyade da ake wa kananan yara a jihar.
Rundunar ‘Yan Sandan jihar Nasarawa ta tabbatar da mutuwar wasu ‘yan Sanda uku dake kwantar da tarzoma a wani kwantan bauna da wasu mahara suka yi musu a mararrabar Udege.
Kungiyar al’ummar Berom dake fadin Jihar Filato ta yi kira ga gwamnatocin tarayya da ta jiha, da su dauki matakan gaggawa wajen dakatar da kashe-kashen da ake yiwa jama’a a wasu sassan jihar.
Hukumar tsaron farin kaya ta Civil Defense a jihar Nasarawa ta yi nasarar cafke wasu mutane dake tafka manyan laifuka, ciki har da wasu da bindigogi a yankin karamar hukumar Toto da ake rikici.
Babban sakataren kungiyar hadin kan Krista ta Najeriya CAN, Rev Dakta Musa Asake ya rasu ranar Juma’a.
Al’ummomin karamar hukumar Doma jihar Nasarawa sun fara zaman sulhu domin neman mafita daga tashe-tashen hankulan da ke faruwa tsakanin manoma da makiyaya, lamarin da rayuka da dama da dukiyoyi sun salwanta.
A kalla mutum 35 ne aka kashe wasu dayawa kuma suka bace a wani harin da ‘yan bindiga suka kai kauyen Tse Umenger dake karamar hukumar Guma a jihar Benue.
Da alama umurnin sufeto janar na 'yan sandan Najeriya na kwace makamai daga hannun jama'a ya fara aiki, yayin da Jihar Filato ta ce ta yi nasarar kwace makamai da harsasai da dama.
Al’umomin Fulani da Tiv a jihohin Benue da Nasarawa, sun bukaci gwamnatocin jiha da na tarayya su sake duba yanayin tsaro a jihohin don tabbatar da zaman lafiya.
Gwamnatin jihar Nasarawa tare da hadin gwiwar hukumar tsaro da kare al’umma ta ‘kasa Civil Defense, sun horas da matasa 5,900 kan yadda zasu samo bayanai daga al’umma don hana afkuwar tashin hankali tun kafin ya afku.
Biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin Fulani da wasu al'ummomin jihar Binuwai wanda ya lakume rayuka da dama ya kuma raba wasu da muhallansu, Shugaba Muhammadu Buhari ya yiwa al'ummar jihar jaje tare da kiran a hada kai a samu zaman lafiya
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya kai ziyara jihar Benue domin jajintawa da kuma kiran jama’a su a zauna lafiya, saboda rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya da jihar ke fama da su.
Cibiyar warkar da cutar yoyon fitsari ta asibitin Jankwano dake Jos ta yi aiki wa mata 451 cikin wannan shekarar kawai kuma kawo yanzu ta warkar da kimanin mata dubu 10
Gwamnatin jihar Filato ta ce zata bunkasa harkar noma don samarwa da al’ummar Najeriya abinci, a cewar gwamnan jihar Simon Lalong, yayin da yake ganawa da manema labarai da nuna musu taraktoci 400 da gwamnatinsa ta sayo don rarrabawa manoman jihar.
Mutane a Karamar Hukumar Bassa sun wayi gari da tsintar gawarwakin mutane uku da suke zargin junansu da kashewa.
Biyo bayan zanga zangar da matuka kekenapep suka yi a Jos jihar Filato da ya kai ga lalata motocin hukumar FRSC tare da raunata wasu jami'anta, gwamnatin jihar ta dakatar da yin sufuri da kekenapep a Jos da Bukuru matakin da yanzu ya jefa talakawa cikin halin kakanikayi