A Najeriya matakan da wasu jihohin suka dauka na kawo karshen ayukkan ta'addanci, musamman katse hanyar sadarwa na ci gaba da jefa jama'a cikin halin Ihun-ka-banza domin ‘yan bindiga na ci gaba da addabar su ba tare da ana jin kukan su ba.
Najeriya tana kawance da wasu kasashen Afirka ta Yamma da wasu kasashe domin saita tsarin kiwo ta yadda watakila hakan zai taimaka wajen magance matsalolin rashin tsaro da kuma habaka arzikin kasashen.
Wata zanga-zangar nuna damuwa akan kara tabarbarewar sha'anin tsaro a garin Isa da ke jihar Sokoto, ta rikide zuwa tarzoma, lamarin da ya yi sanadiyyar kai farmaki tare da kona gidajen kwamishinan lamurran tsaro da kuma na basaraken garin na Isa.
A Najeriya, a daidai lokacin da ake zargin jam'iyar APC mai mulkin kasar da shure umurnin kotu ta gudanar da zabukan shugabanninta a matakin kananan hukumomi, hakan ya sa masana suke ci gaba da bayyana ra'ayoyi mabanbanta.
A Najeriya bisa ga yadda hukumomi a jihohin Arewa ke kakaba dokoki domin neman sauki ga matsalar rashin tsaro, wasu ‘yan kasar na ganin a yi farautar ‘yan bindigar a gama da su zai fi kakabawa mutane dokoki.
A Najeriya masana na ganin cewa halin kuncin rayuwa da jama'a ke fuskanta na daya daga abubuwan da ke saka su jefa rayukan su cikin hadari ba tare da la'akari da illolin da abin zai haifar ba.
A Najeriya alamu na nuna cewa jama'a sun fara debe tsoron ‘yan ta'adda domin suna bayar da gudunmuwa wajen kamawa ko kisan barayin, wanda kuma bai rasa nasaba da ganin cewa hukuma ta kasa magance matsalolin.
A Najeriya masana na ci gaba da tattaunawa akan sahihan hanyoyin da suke ganin su kadai za su iya share fagen inganta sha'anin almajiranci ga gwamnatocin da suka baiwa almajirai mazauni a jihohinsu.
Wannan Talata 10 ga watan Agusta ce ranar daya ga watan Muharram wata na farko a tsarin shekarar Musulunci wanda ya nuna farawar sabuwar shekarar 1443 bayan hijira.
Hukumomin tsaro a jihar sun tabbatar da sakin daliban, sai dai babu wasu bayanai da suka nuna ko an biya kudin fansa.
A Najeriya yadda matsalar rashin tsaro ke kara yawaita na ci gaba da sauya tunanin ‘yan kasar har wasu na ganin hakan kan iya tarwatsa kasar.
Bisa ga yadda hare haren ta'addanci ke ci gaba da jefa rayukan ‘yan Najeriya cikin halin tsaka mai wuya, wasu daga cikin ‘yan kasar na ganin da gwamnatin tarayya za ta baiwa gwamnoni ikon bayar da umurni ga jami'an tsaro da watakila a iya samun saukin matsalolin.
A Najeriya daidai lokacin da mahukunta ke gudanar da bincike akan wani matashi da ake tuhuma da yin kalaman batanci ga fiyayyen halitta, gamayyar kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun ce suna biye da batun da zimmar ganin an yi adalci.
Alamu na nuna cewa ‘yan Najeriya sun fara tunanin ba mafita ga matsalolin da suka dabaibaice kasar illa dukufa ga addu'a tare da komawa Ubangiji, tamkar dai yadda malamai suka yi ta kira a can baya.
A Najeriya wannan Alhamis ce cikar mako biyu da sace daliban sakandare a jihar Kebbi dake arewacin kasar kuma har yanzu shuru ake ji, duk da kalaman da gwamna Abubakar Bagudu ya yi na gayyar shiga daji.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC, ta bankado wasu kamfunan hada-hadar kudade da saka hannun jari ta yanar gizo na bogi.
A Najeriya daidai lokacin da hotunan yaran nan ‘yan makaranta da yan bindiga suka sace suka karade dandalin sada zumunta na yanar gizo, wasu iyayen yaran sun nuna kaduwa tare da kira ga gwamnatin Najeriya da ta yi mai yi wa domin samun fitar da yaran.
A Najeriya jama'a na kyautata zaton cewa rundunar sojin kasar na can na fafatukar ceto daliban makarantar gwamnatin tarayya dake Birnin Yauri wadanda ‘yan bindiga suka sace.
Daidai lokacin jama'a ke alhinin daliban da ’yan bindiga suka sace a Jihar Kebbi, an samu wasu dalibai da suka kubuta daga hannun maharan.
Wani daga cikin iyayen da ke da yara a makarantar Malam Abdulhamid ya ce suna cikin tashin hankali.
Domin Kari