Alamu sun nuna cewa Biden ya dan zubar da hawaye a lokacin da ya hau dandamalin da ya yi jawabin inda aka kwashe sama da minti hudu ana sowa da nuna masa kyakkyawar tarba.
Jam’iyyar Democrat ta fara babban taronta na kasa a ranar Litinin a Chicago inda ake sa ran kusan mutum 50,000 za su isa birnin.
“Babu shakka, kamfanin Zhongshan ya boye wasu bayanai ya kuma yaudari kotun Paris wajen ganin an ba shi wadannan jiragen shugaban kasa wadanda suka je kasar ta Faransa don a duba lafiyarsu.” In ji Onanuga.
Hukumar kididdiga ta NBS a Najeriya ta ce a cikin watan Yulin shekarar 2024, hauhawar farashin kayayyaki ta sauka zuwa kashi 33.40%.
A ranar Laraba asusun na NELFUND ya fitar da karin jerin jami’o’i, makarantun kimiyya da fasaha da kwalejoji 22 da aka tantance don ba dalibansu bashin karatu
Kwararru a fannin tattalin arziki sun ce daukan wannan mataki zai taimaka matuka wajen rage hauhawar farashin mai.
"Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambassada Yusuf Tuggar da sauran mambobin majalisar zartarwarsa za su rattaba hannu kan yarjeniyoyi tare da duba wasu hanyoyi da kasashen biyu za su yaukaka dangatakarsu.”
Ziyarar ta Tinubu mai shekaru 72, na zuwa ne kasa da makonni biyu bayan zanga-zangar tsadar rayuwa da aka yi a kasar wacce ta fi yawan al’uma da karfin tattalin arziki a nahiyar Afirka.
Kazalika wannan shi ne taron kasa na farko da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta tun da ya karbi mulki a watan Mayun 2023.
“A dalilin haka, ana umartar jama’a da su ci gaba da gudanar da harkokinsu cikin walwala a Kaduna da Zaria.” Aruwan ya ce.
“Saboda haka, bari na fada muku kai-tsaye cewa ikirarin da gwamnatin tarayya ta yi akwai kuskure a ciki."
“Ga dukkan alamu, wannan samame da aka kai da daddare mai ban tsoro, wani yunkuri ne na razana 'ya'yan kungiyar." Amnesty ta ce.
Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya yabi rundunar sojin Najeriya da ta bayyana kama sojan da ake zargi da harbe wani matashi mai shekaru 16 a Zaria da ke jihar Kaduna.
A ranar Alhamis za a yi zagayen na semi-finals a filin wasa na Stade de France da ke Paris.
A ranar 5 ga watan Agusta gwamantin ta saka dokar hana zirga-zirga bayan da zanga zangar da ake yi ta jirkice ta koma tarzoma a yankin Jos ta Arewa da kewaye.
Cikin wata sanarwa da ya fitar, Darektan yada labaran rundunar, Manjo Janar Onyema Nwachukwu ya ce ana kan gudanar da bincike kan kisan matashin mai suna Ismail Muhammad.
Domin Kari